JESUS·61 of 61

Invitation to Know Jesus Personally

A narrator gives an invitation to know God personally. The invitation is open to everyone. It means turning to God and trusting Jesus with our lives and to forgive our sins. We can speak to Him in prayer when we're ready to become followers of Jesus.

Ask yours

Bible Quotes

Share
Free Resources

Want to understand the Bible more deeply?

Join our Bible study

Transcript

Hausa ( حَوْسَ)
Cikin littafi mai tsarki Allah ya shaida Almasihu zaizo ya ceci dukkan duniya Rayuwar Yesu ta shaida lallai shi ne annabawa suka yi zancen zuwan sa Annabi Ishaya yace wata budurwa zata yi ciki ta haifi ɗa Bayan shekaru da dama haihuwar Yesu ta cika wannan annabcin Littafi mai tsarki yace mai tsarkin nan da za'a haifa za'ace da shi ɗan Allah Wato za'a kira Yesu ɗan Allah ba ɗa na jikiba amma ɗa na ruhu Hakan ya bayyana ta wurin rayuwarsa Ya warkar da masu cuta Ya gafarta zunubansu ya shirya su da Allah Ya kuma alƙawarta musu mulkin Allah na har abada Ya bada kansa hadaya domin zunuban su ya tashi daga matattu Yesu yace ba me karɓe mini rai don kaina nake bada shi Rayuwar Yesu ta cika annabcin annabawa ta kuma ƙarfafa gaskiyar maganar Allah Annabawa sun shaida cewa Maganar abar dogara ce kuma tabbatacciya ce ya Ubangiji Yesu yace sama da ƙasa zasu shuɗe amma maganata bazata shuɗe ba Yesu ya zo ya bamu rai a yalwace Ganin yadda mutum ya yiwa Allah rashin biyayya a gonar adinin Mutum ya zaɓi bin hanyar sa wacce ta rabasa da mahaliccin sa Littafi mai tsarki yace Ƴan Adam duka sunyi zunubi Sakamakon zunubi kuma mutuwa ne Wato mutuwa ta ruhu kenan Kamar yadda Allah ya tanada rago a maimakon ɗan Ibrahim Haka Allah ya aiko Almasihu ya mutu a madadin mu Rayuwa da mutuwa da tashin sa sun mai da dangantaka tsakanin Allah da masu dogara ga Yesu Yanzu masu bin Yesu ba gafarta zunuban su kaɗai akayi ba Amma an cecesu daga hukunci An tabbatar musu da shiga aljanna Rai da yanci daga ikon zunubi ne Yesu keba kowa a yau Ba bin wani addini ba amma ana zancen gaskata Yesu wanda yace Ganinan tsaye a bakin kofa ina ƙwanƙwasawa Kowa yaji murya ta ya bude kofar sai in shiga wurin sa Ana nufin mu juyo ga Allah mu dogara ga Yesu ya shigo zukatan mu Ya gafarta mana ya maishe mu karɓaɓɓu gareshi ba abin marmari ko tunanin sa a zuciya kaɗai ba Karɓarsa zamu yi da son ran mu ta wurin alheri saboda ban gaskiya Duk wanda keso yazamo mai bin Yesu Almasihu zai iya magana da shi cikin addu'a Mai yuwa kana shirye ka buɗe kofar zuciyar ka zaka iya yin wannan addu'ar a cikin zuciyar ka Ya Yesu Ina bukatarka Nagode da mutuwar da kayi don zunubai na Na furta zunubai na da roƙon gafara Na buɗe zuciyata na karɓe ka kazamo mai ceto na da Ubangiji na Nagode domin gafarar zunubai na domin ka bani rai na har abada Ka maishe ni irin mutumin da ka keso Yanzu da na zamo cikin masu binka Ameen Yesu yayi magana kan masu binsa da cewa Tumaki na sun san murya ta na sansu suna bina In masu bin Yesu suna so su samu rai da ya alkawarta Dole ne suyi addu'a suna karatu da sauraran maganar Allah kullum Suyi ta zumunci da juna suna shaida shi ga wasu Tuna da alƙawarin sa Cewa an mallaka mini iko dukkan sama da ƙasa Gashi ni kuma ina tare da ku har matuƙar zamani
JesusFilm